Home Kanun Labarai Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja zuwa London

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja zuwa London

0
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja zuwa London

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar birnin tarayya Abuja akan hanyarsa ta zuwa birnin Landan na kasar Burtaniya,domin ya gana da likitocinsa.

A ranar Alhamis din makon jiya, Shugaban kasa yayi wata dakatawar ba safai ba akkan hanyarsa daga AMurka zuwa Najeriya, inda ya tsaya a birnin na Landan.

Sai dai kuma, kamar yadda ya fada a shafinsa na Twitter ranar Litinin, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewar zai bar Najeriya ranar Talata domin zuwa Landan da a duba lafiyarsa.