
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar birnin tarayya Abuja akan hanyarsa ta zuwa birnin Landan na kasar Burtaniya,domin ya gana da likitocinsa.
A ranar Alhamis din makon jiya, Shugaban kasa yayi wata dakatawar ba safai ba akkan hanyarsa daga AMurka zuwa Najeriya, inda ya tsaya a birnin na Landan.
Sai dai kuma, kamar yadda ya fada a shafinsa na Twitter ranar Litinin, Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewar zai bar Najeriya ranar Talata domin zuwa Landan da a duba lafiyarsa.