Home Labarai Babu gaskiya a ikirarin Tinubu na baiwa jihohi Biliyan 570 – Gwamna Makinde

Babu gaskiya a ikirarin Tinubu na baiwa jihohi Biliyan 570 – Gwamna Makinde

0
Babu gaskiya a ikirarin Tinubu na baiwa jihohi Biliyan 570 – Gwamna Makinde

Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya musanta ikirarin shugaban kasa Bola Tinubu na cewa gwamnatin tarayya ta bai wa jihohi 36 Naira Biliyan 570 inda ya ce babu gaskiya a bayanin.

A wata sanarwa da Gwamnan ya sanywa hannu kuma aka wallafa ta a shafin gwamnatin jihar a jiya Alhamis, Makinde ya ce kudin da aka bayar ba daga gwamnatin tarayya suke kai tsaye ba.

Gwamnan ya ce kudin da jihohi suka karba, kudin COVID-19 ne daga bankin duniya, inda gwamnatin tarayya ta zama a tsakiya kawai.

Sannan ya ce kudin, an bada su ne domin mayarwa jihohi abinda suka kashe kan cutar COVID-19.

Nairametric