
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai yayi Allah wadai da harin da wasu ‘yan daba suka kaiwa Sanata Suleiman Hunkuyi,Sanata mai wakiltar Arewacin jihar kaduna a majalisar dattawan Najeriya.
Gwamnan ya kuma gargadi dukkan ‘yan daban dake jihar da su sani cewar, Gwamnati ba zata lamunci irin wannan iskanci da keta mutuncin mutane da ‘yan daban suke yi ba.
A yayin da Sanata Hunukyi ke yin wani taron siyasa, ‘yan daba sun kutso kai cikin wajen taron inda suka dinga cewar “Sanata Sai Uba Sani’ wasu kuma na cewar ‘Kaduna Sai Malam’, haka dai matasan suka hargitsa wajen taron, inda suka farwa mutane da sara da suka.
A sanarwar da Gwamna el-Rufai ya bayar ta hannun kakakinsa, Samuel Aruwan, yayi Allah wadai da abinda aka yiwa Sanata Hunkuyi, ya kuma yi jajen abinda ya faru ga sanatan da tawagarsa.