
Tsohon Gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi ya lashe zaben fidda gwanin jam’iyyar APC a yayin da jam’iyyar ke zaben wanda zai yi mata takarar Gwamnan jihar, Fayemi ya lashe zaben ne inda ya kada abokan karawarsa guda 31 inda ya samu kuri’u 941 a cikin 2,337.
Tuni dai baturen zaben jam’iyyar APC a jihar, kuma Gwamnan jihar Nassarawa Umar Tanko Almakura ya bayyana Kayode Fayemi a matsayin wanda ya lashe zaben