
Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje na cikin tsaka mai wuya yayin da majalisar dokokin jihar ya kafa kwamitin bincike kan bidiyon da aka hasko Gwamnan na karbar cin hancin makubadan kudade.
Faifan bidiyon da jaridar Daily Nigerian ta wallahi ya nuna Gwamna Ganduje yana zura kudaden kasar waje a cikin aljihun babbar riga.
Majalisar dokokin jihar Kanon ta kafa kwamitin binciken karkashin jagorancin Baffa Babba DanAgundi tare da wasu mutum shida .