
Gwamnan jihar Binuwai Samuel Ortom ya bayyana cewar ya fice daga jam’iyyar APC bayan abinda ya kira “Jan kati” da jam;iyyar ta bashi.
Ortom ya bayyana hakan ne a ranarLitinin a babban birnin jihar Makurdi jim kadan bayan da ya rantsar da sabbin masu bashi shawara na musamman akan kananan hukumomi Jerome Shimba wanda ya maye gurbin Titus Zam.
A cewarsa, jan katin da jam’iyyar ta bashi, ya bashi damar shiga duk jam’iyyar da yaga dama, wadda ta dace da muradun al’ummar jihar.
Gwamna ya kara da cewar dangantaka tsakaninsa da jam’iyyar da ta bashi damarzama Gwamnan jihar a shekarar 2015 ta yi tsami matuka, ta yadda aka watsarda shi har ya kasance ba shi da jam’iyya.