
Hukumar tsaro ta NSCDC reshen jihar Kano ta ware jami’anta kimanin 3500 domin sanya idanu a zaben kananan hukumomin da za a yi a gobe Asabar.
Wannan na cikin sanarwar da hukumar ta bayar ta hannun kakakin hukumar, Ibrahim Idris wanda ya sanar da hakan ga manema labarai.
“A kalla mutane 3500 ne hukumar tsaro ta NSCDC ta tura domin sanya idanu a zaben kananan hukumomin a jihar Kano” A cewar Mista Idris.
Yace jami’an zasu yi aiki da sauran jami’an tsaro domin zaben na kananan hukumomin jjihar kano, domin yin zabe cikin kwanciyar hankali.