Home Labarai Iyalan Sheikh Dahiru Bauchi sun ƙaryata raɗe-raɗin rasuwar sa

Iyalan Sheikh Dahiru Bauchi sun ƙaryata raɗe-raɗin rasuwar sa

0
Iyalan Sheikh Dahiru Bauchi sun ƙaryata raɗe-raɗin rasuwar sa

Iyalan fitaccen malamin addinin musuluncin nan, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, sun ƙaryata rahotannin da su ka ce ba su da tushe balle makama da aka yada cewar malamin ya rasu.

A safiyar yau Laraba ne aka fitar da jita-jitar cewa Sheikh Dahiru Bauchi, wanda yana daya daga cikin jagororin Darikar Sufanci ta Tijjaniyya a Najeriya ga rasu.

Sai dai kuma a wani martani na gaggawa, Sanusi Dahiru, dan gidan malamin, ya ce, “dan shekaru 97 malamin yana nan lafaiya kalau.

“Mun yi magana da shi kuma yana cikin koshin lafiya a Abuja da safiyar yau.

“Sheikh Dahiru-Bauchi zai bar Abuja zuwa Kaduna gobe (Alhamis) domin rufe Tafsirin Alkur’ani na shekara-shekara, inda ya samu wakilcin dansa, Dakta Sulumbai Dahiru.

“Don haka jama’a a su yi watsi da jita-jitar da ake yadawa cewa Sheikh Dahiru Usman-Bauchi ya rasu.

“Har yanzu yana raye tare da koshin lafiya duk da tsufa”, kuma ya bukaci musulmai masu aminci da su yi addu’a don samun lafiya ga malamin.