Home Kanun Labarai An kashe mutane 42 a wani sabon farmaki da aka kai a jihar Zamfara

An kashe mutane 42 a wani sabon farmaki da aka kai a jihar Zamfara

0
An kashe mutane 42 a wani sabon farmaki da aka kai a jihar Zamfara

‘Yan bindiga sun kashe mutane 42  bayan da suka kaddamar da wani sabon farmaki a wasu kauyuka 18 dake yankin karamar hukumar Zurmi ta  jihar Zamfara. Garuruwan da wannan abu yafi shafa sun hada da Mashema da Kwashabawa da Birane a ranar juma’arda ta gabata.

Sai dai wata majiya ta tabbatar da cewar adadin mutanan da aka kashe na iya kaiwa mutane 100 ko sama da haka, domin iyalai na ta bayar da rahoton rashin ganin ‘yan uwansu.