
‘Yan bindiga sun kashe mutane 42 bayan da suka kaddamar da wani sabon farmaki a wasu kauyuka 18 dake yankin karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara. Garuruwan da wannan abu yafi shafa sun hada da Mashema da Kwashabawa da Birane a ranar juma’arda ta gabata.
Sai dai wata majiya ta tabbatar da cewar adadin mutanan da aka kashe na iya kaiwa mutane 100 ko sama da haka, domin iyalai na ta bayar da rahoton rashin ganin ‘yan uwansu.