
Babbar kotun tarayya dake Kaduna a ranar Laraba ta bayar da umarnin cigabaa da tsare tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Ramalan Yero a gidan kurkuku.
Ramalan Yero da wasu mutum uku suke tssare a hannun hukumar yaki da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa.
Alkalin kotun Mai Shari’ah Muhammad Shuaibu ya bayar da umarnin a cigaba da tsare mutanan har zuwa ranar shida ga watan Yuni.
Daga cikin mutanan da ake tsare da su akwai tsohon Minista Nuhu Wya da tsohon Sakataren Gwamnatin jihar Kaduna, Hamza Danma’awuya da kuma tsohon Shugaban jam’iyyar PDP na jihar Abubakar Haruna.