Home Labarai Mahaukacin kare ya ciji mutane da dama a Kebbi

Mahaukacin kare ya ciji mutane da dama a Kebbi

0
Mahaukacin kare ya ciji mutane da dama a Kebbi

Wani kare da ake kyautata zaton ya sabu tabuwa, ya ciji mutane uku da  dabbobi da dama a kauyen Basaura dake yankin karamar hukumar Jega ta jihar Kebbi.

Daraktan kula da kiwon lafiyar dabbobi na jihar Kebbi, Ahmad Amursa shi ne ya bayyanawa manema labarai hakan a birnin Kebbi ranar Juma’a.

“Wani Kare da ba a san daga ina yake ba kuma ake kyautata zaton cewar tababbe ne ya ciji mutane da dama a kauyen Basaura a karamar hukumar jega”

“karen ya jikkata mutane uku tare da cizon dabbobi da yawa, a sakamakon tabuwa da yayi”