
Daga Hassan Y.A. Malik
Gwamnatin kasar Malaysia a yau Litinin ta fitar da wata doka da nufin kawo karshen yada labaran kanzon kurege a fadin kasar.
Dokar ta yankewa duk wanda ya yada labarin da bashi da majiya ko tushe da gangan zaman gidan kaso na shekaru 10.
Kamfanin dillancin labarai na kasar Faransa ta rawaito cewa kasashe da dama za su kafa irin wannan dokar ta yaki da labaran karya bisa jagorancin Shugaba Donald Trump na Amurka duk kuwa da kalubale da dokar ke samu daga kungiyoyin jama’a na cewa shugabannin kasashen da ke son dabbaka dokar shugabanni ne da ke da sha’awar shimfida kama karya a kasashensu.
Ana zargin Firayi Ministan kasar Malaysia, Najib Razak da kafa wannan doka da nufin yi wa abokan hamayya bita da kulli sakamakon kalubalantarsa da suke yi da wawushe kudade daga baitul malin gwamnati tare
Shugaban ‘yan adawa, Charles Santiago ya bayyana kudirin dokar a matsayin wani makami mai linzami da gwamnati ta fitar don yakar ‘yan adawa a kasar.