
Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi ll ya bayyana cewa bai yi adalci ba ya idan ya soki Shugaba Bola Tinubu kan matsalar tattalin arzikin kasar.
Sai dai Sanusi, ya zargi gwamnatin da ta shude ta Muhammadu Buhari a kan munanan manufofinta na tattalin arziki.
Ya ce gwamnatin Buhari ta yi watsi da shawararsa kan yadda za ta fitar da Najeriya daga matsalolin tattalin arziki.
Kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito, Sanusi, tsohon gwamnan babban bankin Najeriya (CBN), ya yi magana ne yayin wani taron addini da aka gudanar a ranar Lahadi.
Ya ce da gangan yan Najeriya da ke sa ran zai yi magana kan matsalar tattalin arzikin da kasar ke fama da shi ne ke son ya soki Tinubu.