Home Labarai Nan da wasu shekaru ƴan Nijeriya za su dena zuwa ƙasashen waje karatu — Farfesa Gwarzo

Nan da wasu shekaru ƴan Nijeriya za su dena zuwa ƙasashen waje karatu — Farfesa Gwarzo

0
Nan da wasu shekaru ƴan Nijeriya za su dena zuwa ƙasashen waje karatu — Farfesa Gwarzo

Farfesa Abubakar Adamu Gwarzo ya bayyana kwarin guiwar sa na cewa ƴan Najeriya da dama a nan gaba za su daina tafiye-tafiye zuwa kasashen ketare domin samun ingantaccen ilimi.

Dan kasuwa kuma wanda ya kafa jami’ar Canada ta Najeriya da ke Abuja ya yi wannan tsokaci a lokacin da ya ziyarci makarantar.

Gwarzo ya yi nuni da cewa, da karuwar jami’o’i masu zaman kansu a fadin kasar, yawancin ‘yan kasar za su gwammace su yi karatu a gida nan da shekaru kamar ashirin.

Ya ce kishin bunkasa ilimi mai inganci ya sa shi ya kafa jami’ar Maryam Abacha American University of Nigeria da Franco-British International University da ke Kaduna.

“Mun tabbatar da hakan a Kano tare da kafa Jami’ar Maryam Abacha American University of Nigeria, tare da ingantattun tsare-tsare, ingantattun malamai da kuma cancanta.

“Duba yawan ingantattun jami’o’i masu zaman kansu, za ku yarda da ni cewa makomar ilimi tana da haske sosai. A cikin shekaru 20, yawancin ‘yan Najeriya ba za su je wasu kasashe don neman ilimi mai inganci ba, a gida za su samu ilimin da suke nema,” in ji shi.