Home Labarai Nijeriya na zaune a kan wuta, in ji Sarkin Musulmi

Nijeriya na zaune a kan wuta, in ji Sarkin Musulmi

0
Nijeriya na zaune a kan wuta, in ji Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa, Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya bayyana fargabar cewa yayin da miliyoyin matasan Najeriya suka bar aikin yi ba tare da abinci ba, Najeriya na zaune a kan garwashi.

Hakan dai ya zo ne kwanaki biyu da Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya koka kan yadda ake fama da yunwa da fatara a kasar.

Da yake jawabi a wajen taron kwamitin zartarwa karo na 6 na Majalisar Sarakunan Arewa a jiya Laraba a Kaduna, Sarkin Musulmi ya ce matsalar tattalin arzikin da Najeriya ke fama da ita ya kai matakin da ‘yan kasa ke tada jijiyoyin wuya da fushi da yunwa.

Ya ce: “Yanzu mun shiga wani sabon salon shugabanci. Wasu sabbin Gwamnoni sun hau mulki, yayin da wasu ke wa’adi na biyu kuma har yanzu muna fuskantar wadannan matsalolin rashin tsaro.

“Abin da ya fi muni shi ne, muna fuskantar karuwar talauci. Yawancin mutanenmu ba su da hanyoyin rayuwa na yau da kullun.

“Duk da haka, na yi imani magana game da rashin tsaro da karuwar talauci batutuwa biyu ne da ba za mu iya nade hannayenmu ba mu yi tunanin komai yana tafiya daidai. Na sha fadin hakan kuma a fage da yawa cewa al’amura ba sa tafiya daidai a Najeriya kuma tabbas al’amura sun ɓaci a Arewa,” in ji shi.

Ya ce idan har gwamnoni suna son a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihohinsu, su ma su yi aiki da masarautun gargajiya.

“Dole ne mu nemo ayyukan yi ga matasan mu da ke zaman banza kuma na sha fadi haka, muna zaune a kan tsini; matasa masu tarin yawa, miliyoyin su ba su da aikin yi, ba abinci. Muna nemar wa kan mu matsala,” ya yi gargadin.