
Sheikh Dahiru Usman Bauchi fitaccen malamin darikar Tijjaniyya zai yi saukar karatun Tafsirin AlKurani mai girma da yake gabatarwa a jihar kaduna.
A wannan shekarar ne dai kafin karewar wannan wata ake sa ran shehun Malamin zai yi saukar karatun Tafsirin, wanda kuma ita ce karo na uku da za’a sauke karatun tafsiri tun kusan shekaru 39 da ya dauka yana gudanar da Tafsirin a Kaduna.
Bayanai sun bayyana cewar, za’a yi wannan saukar ne a bana, tun bayan wadda aka yi shekaru goma sha biyu (12) da suka gabata da aka yi.
Sheikh Dahiru Usman bauchi dai ya fara gabatar da Tafsirin Alkurani mai tsarki ne tun kusan shekarun 1951, kimanin shekaru 67 da suka wuce.