
Wani rikici ya kunno kai a cikin uwar jam’iyyar APC ta Kasa kan batun hanyoyin da za a bi wajen yin zaben fidda gwani na wadan da zasu tsayawa jam’iyyar takara a mukamai daban daban.
Jagoran jam’iyyar na Kasa Bole Ahmed Tinubu da Shugaban jam’iyyar na Kasa Adams Eric Oshiomhole suka nemi abi wannan tsarin wajen fitar da wadan da zasu wakilci jam’iyyar a matakai daban daban a duk fadin Najeriya.
Sai dai kuma, Geamnonin jam’iyyar karkashin jagorancin Gwamnan jihar Imo Rochas Owelle Okorocha sun ce Sam ba zata sabu ba kan wannan hanya da aka ce za a bi wajen fidda ‘Yan takarkarun Jam’iyyar.
A ranar Alhamis ne dai ake sa ran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar zasu suke zama a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya, domin tabbatar da hanyar da za a bi wajen yin zaben fidda gwani na karshe a cikin jam’iyyar.