Shugaba Buhari ya bar Najeriya zuwa Jordan da Dubai

0
Shugaba Buhari ya bar Najeriya zuwa Jordan da Dubai

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bar Abuja babban birnin tarayyar Najeriya zuwa Amman babban birnin kasar Jordan dan halartar wani muhimmin taro da Sarkin kasar Abdullah ya gayyace shi.

Daga bisani kuma Shugaba Buhari zai bar Amman din zuwa hadaddiyar Daular Larabawa, indai zai halarci wani taron a birnin Dubai.