
Daga Mansur Ahmed
Da ranar yau Jagoran talakawa Dr. Sule Lamido CON, tare da mambobin kwamatin yak’in neman zab’ensa sun ziyarci jihar Zamfara a cigaba da ziyarar jihohin Nigeria 36 domin ganawa da dattawa, shugabannin jam’iyyar PDP da masu ruwa da tsaki game da takarar shugabancin Nigeria a karkashin inuwar jam’iyyar PDP a zaben 2019.
Bayan karb’a ta karamci kamar yadda al’ummomin jihohin Kebbi da Sokoto suka yi masa jiya yayin da ya ziyarce su, jagoran ya ziyarci ofishin jam’iyyar PDP na jiha domin bayyana wannan kuduri ga shugabannin jam’iyyar a matakin jiha da k’ananan hukumomin jihar daga bisani shugaban jam’iyyar ya mara mawa Jagoran baya domin bud’e ofishin yakin neman zabensa na Jihar Zamfara.
Shugaban Jam’iyyar PDP na Jihar Sanata Hassan Nasiha yayin gabatar da jawabinsa ya fara da godiya ga jagoran talakawan bisa tsayawarsa tsayin daka wajen kare mutuncin jam’iyyar PDP a yanayin da ta shiga na fad’uwa zabe da rikicin shugabanci, ya gode masa bisa shawarwari na musamman da zasu amfanar dasu a jihohinsu da yake bayarwa a kowanne lokaci aka hisad’u, yace wajibi ne a yiwa Sule Lamido jinjina ko dan gwarzantaka da juriya da ya nuna Na kasancewarsa a PDP tsawon shekaru 20,
Ya k’ara da cewar al’ummar jihar Zamfara a yanzu suna cikin mummunan yanayi na rashin zaman lafiya da kwanciyar hankali na kashe – kashen rayuka, ya zama kana gidan za’a iya zuwa a kashe ka ko a sakawa garinku wuta, muna neman a taya mu da addu’a kuma ayi mana fatan Allah ya kawo mana shugabancin da zai zama mafita a gare mu a samu zaman lafiya mai dorewa amma wannan shugabancin na APC babu abinda zai iya yi mana
A nasa jawabin Jagoran talakawa Dr. Sule Lamido yace na fara zuwa Zamfara a shekarar 1970 a matsayin d’an kasuwa, kuma Ina da abokai a wannan jihar sosai, maganar zuwa Zamfara a wajena baya matsayin siyasa sai dai matsayin zumunci domin ni naku ne ku nawa ne kuma mu daku amana ce, ba shakka an nuna mana karamci da mutuntawa da karb’a ta musamman kuma kun gode kwarai da gaske
Babu shakka rayuwar mutumin Zamfara tana cikin yanayin damuwa da rashin kwanciyar hankali da farko tukunna Ina addu’ar Allah ya kawo muku zaman lafiya da Nigeria gaba d’aya, a samu kwanciyar hankali da nutsuwa a zuciyar kowa, domin babu wani abu a rayuwar d’an Adam da zai yiwu dole sai da zaman lafiya.
A maganar siyasa a yanzu a matsayin shugabancin APC In akwai dad’i kun sani kuma kuna ji a jikinku in babu dadi ma kun sani, in akwai zaman lafiya kun sani, in akwai fatara, yunwa, talauci, garkuwa da mutane da kisan rayuka ko barazanar rikicin addini kun sani in babu kun sani.
Zab’en 2019 ba zab’e ne tsakanin kirista da musulmi ba, zabe ne tsakanin Musulmi da Musulmi, babu maganar kazo zabe ayi maka kabbara har ana cewa kayi ridda dan aka zab’i PDP, an kira ni kirista, an k’one ofishina, an kone Na Babayo a Azare, an zane Ku da bulala, an kira ni fasto, an kira mu a kowanne irin lafazi haka kawai saboda muna PDP, waliyyai sun hau yanzu ma’asumi yana mulki babu komai sai gilli da mugunta a matsayin hisabi, mutane sun shiga gonar ubangiji wai dole sai sun yi hisabi, a’a mulki a matsayin ramuwa
PDP zata dawo mulki a 2019 da karfin ikon Allah kuma za’a cigaba da inganta rayuwar yan Nigeria fiye da yadda aka yi a baya. Takara ta bata kwalliya bace ko ado ko Neman suna, ko ramuwar gayya, takara ce ta biyan bashin karramawa da adashen da Nigeria ta jefa min a ral