Home Labarai Da Ɗumi-Ɗumi: Tinubu ya sanya hannu kan ƙudirin dokar mafi ƙarancin albashi

Da Ɗumi-Ɗumi: Tinubu ya sanya hannu kan ƙudirin dokar mafi ƙarancin albashi

0
Da Ɗumi-Ɗumi: Tinubu ya sanya hannu kan ƙudirin dokar mafi ƙarancin albashi

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu kan dokar mafi ƙarancin albashi na Naira dubu 70.

Shugaban ƙasar ya sanya hannu ka ƙudurin dokar ne a yau Litinin bayan majalisar wakilai ta amince da ƙudurin.

Dokar dai ta amince da Naira dubu 70 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan kasar nan.

Haka kuma ta amince a dinga bibiyar mafi ƙarancin albashin duk bayan shekaru 3 maimakon shekaru 5 a baya.