Home Labarai Wasikar Malam Aminu Kano zuwa ga Firimiyan Arewa, Ahamadu Bello a 1958

Wasikar Malam Aminu Kano zuwa ga Firimiyan Arewa, Ahamadu Bello a 1958

0
Wasikar Malam Aminu Kano zuwa ga Firimiyan Arewa, Ahamadu Bello a 1958
39 Sudawa,
Akwatin gidan waya 744,
Kano.
8 ga Afrilu 1958.
Zuwa ga Alhaji Ahmadu Sardaunan Sakkwato.
Ina mai farin ciki shaida maka cewa na sadu da wasik’ar ka a ranar 1 ga wannan wata. Hakika, shirye – shiryen ka da suke cikin wannan takardar, babu shakka za su taimaki musulman kasar nan. Allah ya saka maka da mafificin alheri.
Kuma zan yi amfani da wannan dama wajen bayyana maka farin ciki na game da irin karbar da kake yi min, da kuma yadda ka nemi da in tuntube ka a kan duk wani batu da na ji zan iya yi a kan haka. Na tabbata wannan zai amfani abokanta kar mu, wadda muka kulla tun lokacin da ba daya daga cikin mu da ya san zai rike wani mukami a gwamnati. Na yi alkawarin ziyartar ka a duk lokacin da Na zo Kaduna komai kuwa irin yanayin aiyyukana.
A cikin wasikarka na ga ka kawo wani batu da ya dade a raina, Wadda shine ‘yancin kai ga arewacin Najeriya da ma kasa baki daya, ka tuna da abin da na fada maka a cikin jirgin ruwa kan hanyar mu ta zuwa Landan na ce koda yaushe zan goyi bayan ka a kan maganar yancin kai, ka kira ni a duk lokacin da ka bukace ni zan taimaka a duk wata hanya da zan iya. Amma Ina fatan za ka yi nazari a kan shawararin da zan bayar sannan ka kula da wa su tsiraru da za su yi kokarin biyan bukatun kansu da sunan yancin Kai.
Ina fatan zaka sanar da ni a cikin lokaci duk lokacin da bukatar hakan za ta taso saboda yanayin tafiye – tafiye na.
Ina yi maka fatan kammala azumin watan Ramadan lafiya musamman a cikin wannan yanayi Na zafi. Allah ya shirya mana wannan kasa kuma ya daukaka ta.
Naka.
AMINU KANO.