Home Kanun Labarai Wata kotu ta kuma bayar da belin Sambo Dasuki akan Naira miliyan 200

Wata kotu ta kuma bayar da belin Sambo Dasuki akan Naira miliyan 200

0
Wata kotu ta kuma bayar da belin Sambo Dasuki akan Naira miliyan 200

Babbar kotun tarayya dake zama a babban birnin tarayya Abuja ta amince da bayarda belin tsohon mashawarcin Shugaban kasa ta fuskar tsaro Sambo Dasuki mai ritaya akan zunzurutun kudi Naira miliyan dari biyu.

Wannan dai shi ne karo na shida da kotuna daban daban suke bayarda belin Sambo Dasuki mai ritaya, amma harya zuwa lokacin hada wannan rahoto Sambo Dasuki na tsare a hannun hukumar DSS.