Home Labarai Yadda al’ummar garin Sabuwa ke ratsa Kogi don binne mamata

Yadda al’ummar garin Sabuwa ke ratsa Kogi don binne mamata

0
Yadda al’ummar garin Sabuwa ke ratsa Kogi don binne mamata

Daga Yasir Haruna Muhd

Wannan yadda ake kai gawa makabarta kenan a wani kauye da ake kira Sabuwa a Jihar Katsina inda in akayi mutuwa sai an tsallake kogi kafin akai gawa makabarta kamar yadda wani dan’uwa Sadauki dan Ibrahim ya yi korafi sboda rashin hanya sai anbi cimin kogin.

Abin tausayawa musamman a wannan yanayi na damina da muke ciki, ba shakka suna bukatar taimako daga gwamnati musamman ta Jihar Katsina.

Abin lura anan shine:
Yanzu idan ruwa ya cika rafin kenan indai anyi mutuwa sai dai a ajiye gawar har sai ruwa ya ragu yadda za a iya wucewa a kai makabartar ko kuma shikenan sai dai a birne gawan a cikin gari?

Allah Ya sanya wannan kira ta riski wainda alhakin daukan matakin ya rataya a wuyansu, Allah Kuma Ya basu ikon daukar matakin gaggawa.