
Fiye da awaki 100 ne suka mamaye titunan yankin Boise a jihar Idaho da ke kasar Amurka, lamarin da ba a saba gani ba a kasar.
Awakin sun balle ne daga garkensu a ranar juma’a, inda suka shiga gari suna neman abinci.
Awakin sun ja hankalin mazauna Boise inda aka wayi gari da awakin suna kiwo a cikin gari.
An ta yada hutuna da bidiyon awakin a kafafen sada zumunta na Intanet.
Wani a shafin twitter ya ce bayan shekara 30 za su ba jikokinsu labarin yadda awaki suka tsere daga garkensu suka shigo gari.
BBCHAUSA.COM