Home Labarai ‘Yan sanda a jihar Taraba sun gargaɗi mutane kan yaɗa wani bidiyo na batsa

‘Yan sanda a jihar Taraba sun gargaɗi mutane kan yaɗa wani bidiyo na batsa

0
‘Yan sanda a jihar Taraba sun gargaɗi mutane kan yaɗa wani bidiyo na batsa

Rundunar ‘yan sanda a jihar taraba a ranar litinin ta gargaɗi al’ummar jihar kan yaɗa wani hoto bidiyo a shafukan sada zumunta na intanet da yake nuna mace da namiji mazauna birnin jalingo suna saduwa da juna.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, David Misal shi ne yai wannan gargadi a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar. Yace cigaba da yaɗa wannan bidiyo da ake yi a shafukan sada zumunta na intanet bai dace ba, kuma zai iya kawo yamutsi.

Su dai mutanan da aka nuna suna saduwa da juna a bidiyon mazaunan birnin Jalingo ne, abinda yake sanya tsoron kada hakan ya harzuka mutane su tayar da hankali a jihar. Yace, wannan bidiyo ba ga mutanan kadai, yana iya zubar da mutuncin jihar ta taraba.

Lokacin da DALIY NIGERIAN ta tuntubi wani Malamin addinin Musulunci a jihar, Sheikh Aminu Abdullahi ya yi tur da wannan hoton bidiyo tare da yin Allahwadai da masu yaɗa shi, sannan kuma yayi kira ga ‘yan sanda da su takawa yaɗuwar abin birki.

“Ina kira ga dukkan hukumomi a jihar Taraba da su dakile yaɗuwar wannan bidiyo domin hakan bai dace ba a ddinin Musuunci ba da kuma zamantakewa irin ta mutanan Jalingo dama Jihar Taraba baki daya ba, sannan hakan, ya sabawa dokar kasa”

“Kasancewar mutanan da suka yi wannan bidiyo mutanan Jalingo ne, ya zama dole a gurfanar da su gaban kuliya domin a hukuntasu kan wannan batsa da suka aikata, domin hakan ya zama izna ga sauran al’umma”

“Ba zai yuwu ba hukumomi su zuba ido ana cigaba da yaɗa wannan bidiyo a wayoyin hannu, domin hakan na iya bata tarbiyyar yara manyan gobe, hakan kuma babbar illa ne idan aka yi sake yara kanana suka dinga ganin irin wannan bidiyo”

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ne ya ruwaito.