
Daga Hassan Y.A. Malik
Rundunar ‘yan sanda jihar Benuwai ta gurfanar da wasu mutane 28 a gaban kotu kan zargin hada kai wajen kashe wasu Fulani makiyaya guda 10 a jihar.
Fulani makiyayan na cikin fasinjojin da wasu bata gari suka kaiwa hari a ranar Asabar din da ta gabata a kusa da kauyen Yelwata da ke kusa da babbar hanyar Lafia zuwa Markurdi da ke karamar hukumar Guma a jihar.
Lauyan da ke kare wadanda ake zargi, Mr. Tijani Ahmed, a yayin da ake hira da shi ya tabbatarwa da kafafen yada labarai na gidan talabijin din Channels Television da cewa an gurfanar da wadanda ake zargin ne a gaban kotun Majistare da ke birnin Makurdi.
Ya yi kira ga ‘yan sanda da su yi kokarin wajen ganin cewa sun kammala bincikensu a kan lamarin domin kotu ta yi sauren yanke hukunci a kan karar da aka mika ma ta.
Kotu a halin yanzu ta daga saurarar karar zuwa 24 ga watan Afrilu.