
Tsohon Gwamnan jihar Yobe karo uku, kuma sanata mai wakilatar gabashin jihar a majalisar dattawa ta kasa, ya bayyana cewar, zai cigaba da zama a majalisar kasa a matsayin sanata har karshen rayuwarsa.
Tsohon Gwamnan wanda aka zabe shi a matsin sanata tun 2007, inda aka kuma sake zabarsa a shekarun 2011 da kuma 2015.
Alhaji Bukar Abba Ibrahim shi ne shugaban kwamatin kula da zaizayar kasa da sauyin yanayi na majalisar dattawa ta kasa.
Bugu da kari matarsa, Khadija Bukar an zabeta a matsayim ‘yar majalisar wakilai ta kasa har karo uku kafin Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya zabe ta a matsayin karamar ministar harkokin kasashen waje a 2015.
Bai dai bayyana ko zuwa ga wa yayi wannan bayanin ba. Amma dai Gwamnan jihar Yobe me ci Ibrahim Geidam zai kammala wa’adinsa a shekarar 2019 yayin da ake ganin zai nemi kujerar dan majalisar dattawa, wadda suka fito mazaba daya da tsohon gwamna Bukar Abba Ibrahim.
Sanata Bukar Abba a bayyana hakan ne a yayim da yake zantawa da manema labarai a yayin da ake shirin bikin cikar Nigeria shekaru 57 d samun mulkin kai.
Me kuke ganin zai faru tsakanin tsohon gwamna Bukar Ibrahim da Gwamna Ibrahim Geidam a 2019?