Home Labarai 2019: Femi Otedola ya karbi tayin PDP na yin takarar Gwamnan Legas

2019: Femi Otedola ya karbi tayin PDP na yin takarar Gwamnan Legas

0
2019: Femi Otedola ya karbi tayin PDP na yin takarar Gwamnan Legas

Fitaccen attajirin nan kuma Shugaban kamfanin Forte Oil, Femi Otedola ya amsa bukatar jam’iyyar PDP na yi mata takarar Gwamnan jihar Legas a zaben 2019 dake tafe.

Otedola zai yi takara da Akinwunni Ambode Gwamnan jihar Legas na yanzu kuma mai neman wa’adin mulki na biyu a jam’iyyar APC.

Fitaccen dan Jarida Dele Momodu je ya bayyana labarin inda yace Otedola ya tabbatar masa da cewar ya amsa bukatar ta PDP domin yi mata takarar Gwamnan Legas.