Home Labarai Wani rikici mai Nasaba da addini ya barke tsakanin Musulmi da Kirista a jihar Kaduna

Wani rikici mai Nasaba da addini ya barke tsakanin Musulmi da Kirista a jihar Kaduna

0
Wani rikici mai Nasaba da addini ya barke tsakanin Musulmi da Kirista a jihar Kaduna
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufai

Wani rikici da ake kyautata zaton yana da nasaba da addini ya barke tsakanin Musulmi da Kirista a Kasuwar Magani dake yankin karamar hukumar Kajuru dake jihar Kaduna.

Thusday, ta ruwaito faruwar wannan al’amari, inda tace rikicin ya barke da misalin karfe 10 na safe a ranar Litinin.

Rikicin dai ya faru ne sakamakon garkuwa da wata da aka yi kuma aka tursasa mata bin addini a yankin.

Majiyar ta kara da cewar, an bankawa gidaje da dama wuta, yayinda mutane da yawa suka ji munanan raunuka a sakamakon kararwar da aka yi.

Tuni dai aka tura jami’an tsaro domin kwantar da tarzomar da ta barke.