Home Labarai Ramadan: Ƙungiyar Izala ta roƙi Buhari ya buɗe rumbunan abinci

Ramadan: Ƙungiyar Izala ta roƙi Buhari ya buɗe rumbunan abinci

0
Ramadan: Ƙungiyar Izala ta roƙi Buhari ya buɗe rumbunan abinci

 

 

 

 

 

Ƙungiyar Izala ta kasa ta yi kira ga shugaban ƙasa Muhammadu Buhari da ya buɗe rumbunan abinci da kuma rage farashi domin al’umma su ji saukin lamura a watan Ramadan.

Shugaban kungiyar, Sheikh Abdullahi Bala Laune ya yi wannan kira a jiya lokacin buɗe Masallacin Juma’a na ƙungiyar a Abuja.

A wata hira da ya yi da BBC Hausa, Lau ya ce an gina Masallacin ne da kuɗin fatar da jama’a suka bayar a lokacin layya.

Sheikh Bala Lau ya ce ya shaida wa shugaba Buhari wanda ya halarci bikin buɗe Masallacin cewa ya kamata gwamnatinsa ta sa ido ta tabbatar da ba a tsawwala farashin kayayyaki ba.