Home Labarai Fashewar tukunyar gas ta kashe mutane 4 a Kano

Fashewar tukunyar gas ta kashe mutane 4 a Kano

0
Fashewar tukunyar gas ta kashe mutane 4 a Kano

 

A kalla mutane huɗu ne su ka rasu bayan da tukunyar iskar gas ta fashe a unguwar Sabon Gari da ke Ƙaramar Hukumar Fagge a Jihar Kano.

Da ya ke zanta wa da manema labarai a wajen da lamarin ya faru a safiyar yau Talata, Kwamishinan Ƴan Sanda na Jihar, Samaila Shuaibu Dikko ya tabbatar da cewa tukunyar gas ce ta fashe a shagon yin walda.

Ya ce fashewar wacce take mai nauyi ta shafi wani tsohon ginin wata makaranta, inda da wani gini s jikin sa, wanda ya fado wa mutane huɗu daga ciki su ka mutu.

Ya ce yanzu haka a na ci gaba da duba ƙuraguzan ginin domin ko za a gano wasu da ya danne.

Ya kuma ƙaryata raɗe-raɗin da a ke yi cewa fahdear bam ce, inda ya tabbatar da cewa tukunyar gas ce ta fashe.