Home Siyasa Kotu ta dakatar da shugabanncin PDP ɓangaren Sagagi a Kano

Kotu ta dakatar da shugabanncin PDP ɓangaren Sagagi a Kano

0
Kotu ta dakatar da shugabanncin PDP ɓangaren Sagagi a Kano

 

Wata Babbar Kotun Taraiya da ke zaman ta a Kano ta dakatar da shugabancin jam’iyar PDP, ƙarƙashin Shehu Sagagi har sai ta gama sauraron ƙarar da a ka shigar a gaban ta.

Ana zargin Sagagi da biyayya ga tsohon gwamnan jihar kuma shugaban jam’iyar NNPP na ƙasa, Rabi’u Kwankwaso.

Wani Bello Bichi ne ya shigar da ƙarar a gaban Mai Shari’a A. M. Bichi, inda ya yi ƙarar PDP, INEC da sauran mutane 40.

Kotun ta ce ta bada umarnin ne domin gujewa wani yanayi da za a zama babu shugabci a jam’iyar, shi ya sanya ta bada umarnin ga wanda a ke ƙara na 3 har zuwa na 42.