Home Labarai Hukumar Shari’a ta Kano ta aurar da mata biyu da su ka musulunta

Hukumar Shari’a ta Kano ta aurar da mata biyu da su ka musulunta

0
Hukumar Shari’a ta Kano ta aurar da mata biyu da su ka musulunta

 

 

 

 

Hukumar Shari’ar ta Jihar Kano ta aurar da wasu da su ka musulunt, inda ta ɗauki nauyin bikinsu; ta sai musu gadaje da sauran kayan ɗaki da na kicin.

Daraktan Gudanarwa da Ayyuka na hukumar, Auwal Lamido, ya shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN a yau Alhamis a Kano, inda ya ce Hukumar ta kuma warware wasu rikice-rikice bakwai da suka shafi rikicin shugabancin masallatai da makarantun Islamiyya cikin watanni biyu.

A cewar daraktan, an warware matsalolin a watan Maris da Afrilu.

Malam Lamido ya bukaci jama’a da su tabbatar da cewa su na aiwatar da ɗabi’u masu kyau da kuma tsoron Allah a cikin mu’amalarsu.

An kafa hukumar ne a shekara ta 2001 a matsayin ofishin kula da harkokin zamantakewa na Musulunci, amma sai a ka ɗaga likkafarta zuwa Hukumar Shari’a a ranar 7 ga Nuwamba, 2003.

Aikinta shi ne ingantawa, aiwatarwa da kuma inganta ɗabi’un Musulunci da na al’adu a cikin jihar.