Home Labarai A sakar mini Nnamdi Kanu a hannu na, Gwamna Soludo ya roƙi gwamnatin tarayya

A sakar mini Nnamdi Kanu a hannu na, Gwamna Soludo ya roƙi gwamnatin tarayya

0
A sakar mini Nnamdi Kanu a hannu na, Gwamna Soludo ya roƙi gwamnatin tarayya

Gwamnan jihar Anambra, Farfesa Chukwuma Soludo, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta sakin jagoran masu fafutukar kafa kasar Biyafara (IPOB), Nnamdi Kanu, ba tare da wani sharadi ba, yana mai cewa a shirye yake ya tsaya a masa a matsayin garano ga shugaban na kungiyar IPOB da aka tsare.

Soludo ya bayyana haka ne a lokacin kaddamar da yakin neman zaben jam’iyyar APGA, wanda ya shaida halartar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Farfesa Peter Umeadi da sauran ƴan takarar jam’iyyar a jihar da kuma Kudu maso Gabas.

Ya ce: “Ina kira ga gwamnatin tarayya da ta saki Mazi Nnamdi Kanu ba tare da wani sharadi ba. Idan ba za a iya sakin shi ba tare da wani sharadi ba, ina so a sake shi a gare ni, kuma zan tsaya masa a matsayin garanto.

“Muna bukatar Nnamdi Kanu a tattaunawar da za a yi domin tattauna matsalar rashin tsaro a yankin Kudu maso Gabas. Dole ne mu kawo karshen rashin tsaro a yankin Kudu maso gabas kuma muna bukatar Nnamdi Kanu ya kasance a kusa.

“A wasu lokutan da suka gabata mun kafa kwamitin gaskiya da sasantawa domin gano musabbabin rashin tsaro a yankin Kudu maso Gabas kuma sun kusa kammala aikinsu.

“Amma wannan batu na rashin tsaro ba za a iya magance shi da kyau ba tare da kawo manyan ‘yan wasa a wannan lamarin ba.

“Mun yi amfani da tsarin motsa jiki da rashin kishin kasa wajen yaki da rashin tsaro a yankin Kudu maso Gabas, amma ba za a iya kammala tsarin ba tare da gwamnatin tarayya ta saki Mazi Nnamdi Kanu ba.