
Rundunar ‘yansandan jihar Kogi a tsakiyar Najeriya ta tabbatar da mutuwar biyu daga cikin ɗaliban nan da ‘yanbindga suka yi garkuwa da su a Jami’ar Kimiyya ta Osare.
Rundunar ta bayyana kisan daliban a matsayin abin takaici, ta kuma sha alwashin tabbatar da ceto sauran ɗaliban da maharan ke ci gaba da garkuwa da su.
A ranar 13 ga watan Mayu ne maharan suka sace ɗaliban bayan da suka yi wa jami’ar tasu dirar mikiya a lokacin da suke tsaka da karatun fara jarabawa.
BBC Hausa