Home Labarai Ƴan bindiga sun kashe biyu cikin ɗaliban jami’ar Kogi da suka sace

Ƴan bindiga sun kashe biyu cikin ɗaliban jami’ar Kogi da suka sace

0
Ƴan bindiga sun kashe biyu cikin ɗaliban jami’ar Kogi da suka sace

Rundunar ‘yansandan jihar Kogi a tsakiyar Najeriya ta tabbatar da mutuwar biyu daga cikin ɗaliban nan da ‘yanbindga suka yi garkuwa da su a Jami’ar Kimiyya ta Osare.

Rundunar ta bayyana kisan daliban a matsayin abin takaici, ta kuma sha alwashin tabbatar da ceto sauran ɗaliban da maharan ke ci gaba da garkuwa da su.

A ranar 13 ga watan Mayu ne maharan suka sace ɗaliban bayan da suka yi wa jami’ar tasu dirar mikiya a lokacin da suke tsaka da karatun fara jarabawa.

BBC Hausa