Home Labarai Zan fitar da al’ummar Tudunwada kunya, in ji Sa’adatu, mace ciyaman ta farko a tarihin Kano

Zan fitar da al’ummar Tudunwada kunya, in ji Sa’adatu, mace ciyaman ta farko a tarihin Kano

0
Zan fitar da al’ummar Tudunwada kunya, in ji  Sa’adatu, mace ciyaman ta farko a tarihin Kano

Hajiya Sa’adatu Salisu Yushau, zaɓaɓɓiyar shugabar ƙaramar hukumar Tudunwada ta karbi rantsuwar kama aiki.

Hajiya Sa’adatu na daya daga cikin ciyamomi 44 da gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya rantsar a yau Asabar a gidan gwamnatin jihar.

A hirar ta da wakilin DAILY NIGERIAN HAUSA, Hajiya Sa’adatu ta ce kasancewar ta mace ɗaya tilo kuma ta farko a tarihin jihar Kano da ta zama shugabar ƙaramar hukuma, za ta yi kokari ta ciyar da Tudunwada gaba.

A cewar ta, “duk abinda namiji zai iya mace ma za ta iya”, saboda haka ta ce za ta dage ta ga ta yi bajintar da ba a taba yi ba a ƙaramar hukumar Tudunwada.

Ta ce ta ma da yaƙinin da taimakon Allah da kuma daukacin al’ummar Tudunwada, za ta sauke nauyin da aka dora Mata wajen inganta rayuwar al’ummar yankin.