Home Kanun Labarai Paul Biya dan shekaru 85 ya sake cin zaben Shugaban kasa a Kamaru

Paul Biya dan shekaru 85 ya sake cin zaben Shugaban kasa a Kamaru

0
Paul Biya dan shekaru 85 ya sake cin zaben Shugaban kasa a Kamaru

A kasar Kamaru An sake zaben Paul Biya dan shekaru 85 a matsayin Shugaban kasa karo na 7 a jere.

Tuni dai hukumar zaben kasar ta bayyana Shugaba Biya a matsayin wanda ya lashe zaben Shugaban kasar wanda yayi Nasara da kashi 71.2.

Amma jagoranci ‘Yan adawa kasar a birnin Yawunde da Duwala sun yi kira da a soke zaben kuma a sake yinsa. Abinda hukumar zaben kasar tayi fatali da shi.