
Gwamnan jihar Nassarawa Umar Tanko Amakura ya baiwa hukumar Yaki da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC kyautar fili mai fadin hekta 50 a lafiya babban birnin jihar.
Sai dai kuma tsohon Antoni janar kuma kwamishinan Shariah na jihar ya bayyana cewar wannan kyautar fili ta sabawa doka da kundin tsarin mulkin Najeriya.