Home Labarai Sifeton ‘Yan sanda na kasa ne ke da alhakin duk abinda ya same ni – Saraki

Sifeton ‘Yan sanda na kasa ne ke da alhakin duk abinda ya same ni – Saraki

0
Sifeton ‘Yan sanda na kasa ne ke da alhakin duk abinda ya same ni – Saraki

Shugaban Majalisar dattawa ya kasa Bukola Saraki ya kalubalanci ‘Yan sanda a lokacin da suke baiwa ‘yan daba da suka farmasa kariya a Ilorin babban birnin jihar Kwara.

Haka kuma, Saraki ya kalubalanci Sifeton ‘Yan sanda na kasa akan yadda yake shiga harkar abinda ya Shafiu jihar Kwara musamman a Siyasance.

A saboda haka, Saraki ya bukaci ‘Yan Najeriya da su kalubalanci Sifeton ‘Yan sanda akan duk abinda ya shafe shi shi da iyalansa.

Saraki na yin wannan bayani ne a shalkwatar yakin neman zaben dan takarar jam’iyyar PDP ta kasa dake Abuja yayin da yake ganawa da manema labarai.