Home Labarai Afghanistan na duba yiwuwar barin mata su yi karatun jami’a

Afghanistan na duba yiwuwar barin mata su yi karatun jami’a

0
Afghanistan na duba yiwuwar barin mata su yi karatun jami’a

Wani kwamiti na ma’aikatar ilimi mai zurfi ta Afganistan ya ce yana kan shirin sake bude jami’o’i ga dalibai mata, kamar yadda kafafen yada labarai na kasar suka ruwaito a yau Litinin.

Kwamitin ya bayyana hakan ne a lokacin wani rahoto na shekara-shekara na ma’aikatar.

“Za mu raba shi ga jama’a idan an kammala shirin,” in ji rahoton.

Mukaddashin ministan ilimi mai zurfi, Lutfullah Khairkhwa ya ce har yanzu ba a bayyana lokacin kammala shirin ba.

Ya zuwa yanzu dai an hana mata shiga jami’o’i a kasar Afganistan.

Ma’aikatar Ilimi mai zurfi ta sanar da hana ilimin mata a watan Disambar 2022.