Home Kanun Labarai Boko Haram sun dawo da ‘yan matan Dapchi da suka sace

Boko Haram sun dawo da ‘yan matan Dapchi da suka sace

0
Boko Haram sun dawo da ‘yan matan Dapchi da suka sace

Rahotanni daga garin Dapchi da safiyarnan sunce ‘yan kungiyar Boko Haram da suka sace ‘yan matan makarantar Sakandiren Gwamnati a Dapchi din sun dawo da su.

Wani da ya ga lokacin da aka dawo da ‘yan matan, ya shaida mana cewar yaga manyan motoci guda shida suna ajiye ‘yan matan a cikin garin na Dapchi. Sannan kuma,motocin da suka ajiye ‘yan matan sun wuce sun tafi ba tare da an kama su ba.

Zamu kawo cikakken bayani zuwa anjima.