
Mataimakin Shugaban kasa, Yemi Osinbajo ya bayyana cewar Gwamnatin tarayya karkashin jagorancin Shugaba Buhari ta kashe sama da Naira Tiriliyan guda domin inganta rayuwar ‘yan Najeriya.
Osinbajo ya bayyana hakan ne a ranar Asabar, inda yace Gwamnatin ta mayarda hankali sosai wajen ayyukan raya kasa da suka hada da gina hanyoyi da aikin layin dogo da kuma taimakawa rayuwar matasa, musamman ta bangaren aikin N-Power.
Mataimakin Shugaban kasar ya kara da cewar ya zuwa yanzu bliyoyon kudade aka kashe wajen ciyarda daliban Firamare abinci kyauta a makarantunsu, wanda Gwamnatin Buhari ce ta bullo da wannan shiri na ciyar da dalibai abinci kyauta.
Ko me zaku ce kan wannan batu?