
Ga dukkan alamu, Shugaban Kwamitin Riƙo na Jam’iya mai mulki APC kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni ne zai jagoranci babban taron APC na ƙasa a ranar 26 ga watan Maris.
Jaridar Punch ta jiyo cewa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya umarci Buni ɗin da ya jagoranci taron, amma ya masa zazzafan kashedi cewa ba za a ƙara ɗage ranar yin Babban taron jam’iyar na ƙasa ba.
Majiyoyi sun shaida wa Punch cewa Buhari ya ɗauki wannan matakin ne bayan ganawa da ya yi da wasu jiga-jigan jam’iyar a Landan.
Da ga cikin waɗanda su ka baiwa Buharin shawarar ɗaukar wannan matakin akwai Antoni-Janar kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, wanda ya nuna wa shugaban ƙasar illar da za a iya samu ta ɓangaren Shari’a.
Haka-zalika an jiyo cewa, bayan da a yanzu shugaban ƙasar ya nuna ba shi da wani ɗan takara a zaben shugaban jam’iyar na dindindin, yanzu gurbin ya zamto a bude, inda kowa zai iya nema.
Hakan kuma, in ji majiyoyi, ya nuna rashin tabbas a kan rabon muƙamai na shiyya-shiyya da jam’iyar ta fitar a makon da ya gabata.
Haka kuma a ganawar ta birnin Landan, Buhari ya musanta bada umarnin cire Buni da kuma maye gurbinsa da Gwamna Abubakar Sani Bello kamar yadda Gwamna Nasir El-Rufai ya faɗa.