Home Labarai Dangote ya ƙaddamar da shirin samar da abinci mai gina jiki a Kano

Dangote ya ƙaddamar da shirin samar da abinci mai gina jiki a Kano

0
Dangote ya ƙaddamar da shirin samar da abinci mai gina jiki a Kano

 

Gidauniyar Aliko Dangote (ADF) ta fara aiwatar da shirinta na samar da abinci mai gina jiki mai taken: Aliko Dangote Foundation Integrated Nutrition (ADFIN) a Jihar Kano.

A cewar Daraktan Lafiya da Abinci na Gidauniyar, Dakta Francis Aminu, ya ce shirin ya yi dai-dai da shirin yin amfani da sabbin tsarin cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko da aka gwada a fadin ƙananan hukumomin 5, wannan na a matsayin tsarin kula da marasa lafiya da Kuma Masu fama da tamowa.

A halin da ake ciki, an horar da ma’aikatan lafiya sama da 30 domin gudanar da shirin a Kano.

Dakta Aminu ya ce an gudanar da shirin horon na kwanaki 5 tsakanin 17 zuwa 22 ga Disamba 2021.

“Maƙasudin bayar da horon shi ne baiwa ma’aikatan lafiya dabarun da ake bukata kan tantancewa da kula da yara ‘yan kasa da shekaru biyar masu fama da tamowa. Horon na kwanaki 5 ya baiwa mahalarta damar samun Ilimi mai zurfi wanda yayi dai-dai da tsarin bada horo Hukumomi kula da tamowa ta Kasa, “in ji shi.

Ya ce mahalarta taron sun fito ne daga ma’aikatar lafiya ta jiha da kuma guda biyar ADFIN da aka tallafa daga kananan hukumomin Bebeji, Dala, Kura, Tudun Wada, da Rimin-Gado da suka hada da jami’an tsaro (OICs), ma’aikatan lafiya na al’umma (CHEWs).

Jami’an kula da abinci mai gina jiki, masu kula da lafiyar mata da yara (MCH), da Jami’an kula da Lafiya a matakin Farko (PHC).

Kwamishinan lafiya na jihar Kano Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa ne ya buɗe taron horaswar, wanda ya samu wakilcin babban sakatare a ma’aikatar lafiya ta jihar Kano, Hajiya Amina A Musa.

A jawabinsa na rufe taron, Kwamishinan ya yabawa kwazon Shugabannin Ma’aikatar kula da Lafiya a matakin Farko tare da ma’aikatansu Sakamakon juriyar da suke Yayin kwanaki 5 da akai ana basu horon.

Daga nan sai ya yabawa gidauniyar bisa gudunmawar da take bayarwa wajen Gudanar da aiyukan Gina al’umma a Najeriya, da ma nahiyar Afrika baki daya, Sannan Kuma ya bayyana matukar jin dadinsa bisa ga dimbin gudunmawar da Alhaji Aliko Dangote yake bayarwa a jihar Kano.