Home Labarai Dangote ya mallakawa BUK wani katafaren gini na biliyoyin kudi

Dangote ya mallakawa BUK wani katafaren gini na biliyoyin kudi

0
Dangote ya mallakawa BUK wani katafaren gini na biliyoyin kudi
Alhaji Aliko Dangote

A kokarinsa na taimakawa al’umma wajen ganin an koyawa mutane sana’o’i domin fita daga cikin halin kangin talauci, fitaccen attajirin nan Alhaji Aliko Dangote, ya mallakawa jami’ar Bayero dake Kano, wani katafaren gini da kimarsa takai naira biliyan 1.2, domin horar da mutane kan ilimin kasuwanci da sana’a.

Wannan katafaren gini da Alikoo Dangote yayi, za’a yi bikin mika shi zuwa ga jami’ar Bayero a wata mai zuwa, kuma a lokacin ne ake sa ran fara amfani da shi wajen koyarwa a fannin kasuwanci da kuma sana’a.

Wannan gini irinsa ne na farko a kafatanin jami’o’in dake Arewacin Najeriya. haka nan kuma, Alhaji Aliko Dangote na gia wani makekekn gini makamancin wannan, a jami’ar birnin Badun dake jihar Oyo a yankin kudu maso yammacin Najeriya.

Gidauniyar Aliko Dangote ce dai ta dauki gabarar wannan ayyuka domin bayar da tasa gudunmawar wajen inganta rayuwar al’umma, ta hanyar tallafa musu wajen samun ilimin sana’a da kuma na kasuwanci domin tafiya daidai da zamani.

Binciken DAILY NIGERIAN ya tabbatar cewar, wannan kaafaren gini na BUK ya kunshi, babban dakin taro da dakunan daukar darasi da azujuwa da dakin karatu da ofisoshin Malamai da sauransu.