Home Labarai Duk wanda Hisbah ta kama ya na aikata munanan ɗabi’u cikin Ramadan to zai ɗanɗana kuɗarsa — Ibn-Sina

Duk wanda Hisbah ta kama ya na aikata munanan ɗabi’u cikin Ramadan to zai ɗanɗana kuɗarsa — Ibn-Sina

0
Duk wanda Hisbah ta kama ya na aikata munanan ɗabi’u cikin Ramadan to zai ɗanɗana kuɗarsa — Ibn-Sina

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta yi barazanar hukunta duk waɗanda aka kama su na aikata munanan ɗabi’u a wannan wata mai tsarki na Ramadana.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Ibrahim Lawan ya fitar ranar Alhamis a Kano.

Ya ce Shugaban na Hisbah, Dakta Harun Ibn-Sina ya bayyana cewa wadanda suke aikata munanan dabi’u a cikin wannan wata mai alfarma, za a yi maganinsu.

“Wasu daga cikin matasan da ke cin abinci a bainar jama’a a lokacin azumi su ma ba za su tsira ba,” inji shi.

Malam Ibn-Sina ya yi kira ga jama’a da su taimaka wa marayu da mabukata, a wani yunkuri na ba da taimako ga radadin da suke ciki.

Ya kuma bayyana cewa Hisbah za ta tura jami’anta zuwa masallatai domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a cikin watan Ramadan.

Babban kwamandan hukumar, ya ce: “Rundunar Hisbah za ta ziyarci masallatai a lokutan buda baki, Tarawihi, Sallar Tahajjud domin kare masu ibada da dukiyoyinsu daga rashin kishin kasa.