Home Labarai Ganduje ya danƙawa Gawuna kujerar mulki yayin da gwamnan ya tafi ɗaukar kwas a jami’ar Havard

Ganduje ya danƙawa Gawuna kujerar mulki yayin da gwamnan ya tafi ɗaukar kwas a jami’ar Havard

0
Ganduje ya danƙawa Gawuna kujerar mulki yayin da gwamnan ya tafi ɗaukar kwas a jami’ar Havard

 

Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya tafi Ƙasar Amurka domin ɗaukar wani kwas na mako ɗaya a jami’ar Havard.

Wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai, Muhammad Garba ya fitar ta ce gwamnan ya tafi ne domin yin wani kwas mai taken “Sahihiyar hanyar bunƙasa harkar mulki” a makarantar koyon harkar kasuwanci ta jami’ar Havard da ke Boston.

Sanarwar ta ce Ganduje ya danƙa ragamar mulki da cikakken iko ga mataimakinsa, Nasiru Gawuna a matsayin gwamnan riƙon-ƙwarya.

Sanarwar ta ƙara da cewa, gwamnan ya bada umarnin cewa duk wata hada-hadar kuɗi a kaiwa ofishin mataimakin gwamnan domin yin abinda ya dace.