Home Labarai Gwamna Fayose na Ekiti yace Allah ne ya bashi umarni ya zabi mataimakinsa a matsayin wanda zai gaje shi

Gwamna Fayose na Ekiti yace Allah ne ya bashi umarni ya zabi mataimakinsa a matsayin wanda zai gaje shi

0
Gwamna Fayose na Ekiti yace Allah ne ya bashi umarni ya zabi mataimakinsa a matsayin wanda zai gaje shi

Gwamnan jihar Ekiti Ayodele Fayose, a wajen wani gangami da jam’iyyar PDP ta shirya a Ado-Ekiti, ya bayyana cewar,Allah ne ya umarce shi da ya zabi mataimakinsa, Kolapo Olusola Eleka a matsayin wanda zai gajeshi.

“Olusola bai taba tunanin zai zama mataimakin Gwamna ba, Amma Allah ya umarce ni da na dauke shi ya zamar min matamaiki, na gaya masa idan wa’adinmu ya kare tare zamu sauka, amma saai Allah yace na zabe shi a matsayin wanda zai gaje ni” Fayose ya fada a gaban jama’a.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya, NAN, ya ruwaito cewar, tsohon ministan ayyuka da gidaje, Dayo Adeyeye, da Sanata Biodun Olujimi da wani jakadan Najeriya a Kanada Dare Bajide duk sun nuna sha’awarsu ta neman tsayawa gwamnan jihar a jam’iyyar ta PDP a zaben da za’a yi 14 ga watan Yuli.

Sai dai wani Kwamishina a Gwamnatin ta fayose, Owoseeni Ajayi, yayi tutsu kan batun zabar Olusola a matsayin dan takarar jam’iyyaar ta PDP.Indaa ya bayyana hakan da cewar tsabar rashin adalci ne.

NAN