Home Labarai Gwamnan Kogi na tuhumar Sarki Ohinoyi na Ebira bisa ƙin zuwa tarbar Buhari

Gwamnan Kogi na tuhumar Sarki Ohinoyi na Ebira bisa ƙin zuwa tarbar Buhari

0
Gwamnan Kogi na tuhumar Sarki Ohinoyi na Ebira bisa ƙin zuwa tarbar Buhari

Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya aike wa Sarki Ohinoyi na Ƙasar Ebira, Abdulrahman Ado Ibrahim, takardar tuhuma bisa ƙin tarbar Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a ziyarar aiki da ya kai a jihar a ranar 29 ga watan Disamba.

Gwamnatin jihar, a takardar tuhuma da ta aike wa Sarkin, mai ɗauke da sa hannun daraktan harkokin masarautu na jihar, Enimola Eniola, mai kwanan wata 5 ga watan Janairu, ta ce abinda Sarkin ya aikata ka iya zubar da mutuncin jihar Kogi, musamman ma ƙasar Ebira a idon duniya.

Gwamnatin ta suffanta abinda Sarkin ya yi a matsayin rashin biyayya da ɗa’a ga gwamnati.

A takardar, gwamnatin ta buƙaci Sarki Ibrahim da ya bada hakuri a cikin sa’o’i 48 sannan ya faɗi dalili gamsasshe da ya sa ya ƙi zuwa tarbar shugaban ƙasa.