Home Labarai Gwamnatin Kaduna ta ƙaryata rahoton sace mutane a kan titin Abuja-Kaduna

Gwamnatin Kaduna ta ƙaryata rahoton sace mutane a kan titin Abuja-Kaduna

0
Gwamnatin Kaduna ta ƙaryata rahoton sace mutane a kan titin Abuja-Kaduna

Gwamnatin jihar Kaduna, ta ce labarin sace mutane a hanyar Abuja zuwa Kaduna karya ne kuma farfaganda ce.

Kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida Samuel Aruwan ne ya karyata labarin a wata sanarwa da ya fitar a jiya Juma’a a Kaduna.

Aruwan ya ce, “rahoton da wata jarida ta wallafa a yau, wanda ke zargin cewa ‘yan bindiga sun yi garkuwa da dimbin al’umma a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna karya ne kuma farfaganda ce, domin ba a samu irin wannan lamari a babbar hanyar da ta ratsa kananan hukumomi biyar na Kaduna da Neja ba.

“Daga bayanan da ake da su, lamarin bai faru a Iche ba kamar yadda kafafen yada labarai suka ruwaito.

“Gwamnati na kallon rahotannin a matsayin mara sa inganci da wasu batagari su ka yaɗa a matsayin babbar illa ga yakin da ake yi da ƴan bindiga da kuma yadda jami’an tsaro ke gurfanar da su a gaban kuliya, a cikin kasadar rayuwarsu,” in ji shi.

Kwamishinan ya ce gwamnati na bin diddigin jami’an tsaro kan duk wani abu da ya shafi tsaro da lafiyar al’umma.